an-Nasr (النَّصْر)

Abubakar Mahmoud Gumi by Abubakar Mahmoud Gumi

Chapter 110 • 3 verses • Meccan

110:1 Idan taimakon Allah ya zo da cin nasara.
110:2 Kuma ka ga mutane suna shiga addinin Allah, ƙungiya-ƙungiya.
110:3 To, ka yi tasbihi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka nẽme Shi gafara, lalle Shi (Ubangijinka) Ya kasance Mai karɓar tũba ne.