68:1
                                        
                                    
                                    Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:2
                                        
                                    
                                    Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:3
                                        
                                    
                                    Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:4
                                        
                                    
                                    Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:5
                                        
                                    
                                    Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:6
                                        
                                    
                                    Ga wanenku haukã take.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:7
                                        
                                    
                                    Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:8
                                        
                                    
                                    Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:9
                                        
                                    
                                    Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:10
                                        
                                    
                                    Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:11
                                        
                                    
                                    Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:12
                                        
                                    
                                    Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:13
                                        
                                    
                                    Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:14
                                        
                                    
                                    Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:15
                                        
                                    
                                    Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:16
                                        
                                    
                                    Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:17
                                        
                                    
                                    Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:18
                                        
                                    
                                    Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:19
                                        
                                    
                                    Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:20
                                        
                                    
                                    Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:21
                                        
                                    
                                    Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:22
                                        
                                    
                                    Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:23
                                        
                                    
                                    Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:24
                                        
                                    
                                    "Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:25
                                        
                                    
                                    Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:26
                                        
                                    
                                    Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:27
                                        
                                    
                                    "Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:28
                                        
                                    
                                    Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:29
                                        
                                    
                                    Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:30
                                        
                                    
                                    Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:31
                                        
                                    
                                    Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:32
                                        
                                    
                                    "Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:33
                                        
                                    
                                    Haka dai azãbar take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:34
                                        
                                    
                                    Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:35
                                        
                                    
                                    Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:36
                                        
                                    
                                    Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:37
                                        
                                    
                                    Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:38
                                        
                                    
                                    Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:39
                                        
                                    
                                    Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:40
                                        
                                    
                                    Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:41
                                        
                                    
                                    Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:42
                                        
                                    
                                    Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujũda, sai bã zã su iyãwa ba.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:43
                                        
                                    
                                    Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:44
                                        
                                    
                                    Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:45
                                        
                                    
                                    Ina jinkirtã musu, lalle kaidiNa mai ƙarfi ne.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:46
                                        
                                    
                                    Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:47
                                        
                                    
                                    Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:48
                                        
                                    
                                    Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:49
                                        
                                    
                                    Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:50
                                        
                                    
                                    Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:51
                                        
                                    
                                    Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            68:52
                                        
                                    
                                    Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.